IQNA

Adadin Falastinawan Da Suka Jikkata A Masallacin Quds Ya Karu

23:29 - May 09, 2021
Lambar Labari: 3485895
Tehran (IQNA) adadin Falastinawan da suka jikkata farmakin da Isra'ila ta kaddamar a kan masallacin Quds a jiya yana karuwa.

Hukumar Agajin gaggawa ta Falastinu wato Helal Ahmar ta bayar da bayanin cewa, karin Falasdinawa 90 ne suka jikkata a harabar Masallacin Kudus da sauran wurare a birnin Kudus yayin da jami’an tsaron Isra’ila ke ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri kan Falasdinawa.

Hukumar bayar da agajin gaggawar ta sabunta alkaluman a safiyar yau Lahadi, inda ta ce wadanda suka jikkata sun hada da mutane 23, wadanda aka kwantar a asibiti, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na reuters ya ruwaito.

Tun da farko dai an rawaito cewa kimanin Falasdinawa 205 ne suka samu rauni a ranar Juma’a bayan da sojojin Isra’ila suka farma daruruwan Falasdinawa dake ibada a harabar masallacin na Kudus, da harsasai na roba, da hayaki mai sa hawaye, da kuma gurnet mai tsananin kara.

Kasashen musulmi da dama da suka hada da Iran, Turkiyya, Masar, Kuwait, duk sun yi tir da farmakin na Isra’ila kan Falasdinawan dake ibada a harabar masallacin na Kudus.

برپایی مراسم اعتکاف مسجد الاقصی با حضور 90 هزار فلسطینی/زخمی شدن 100 نفر دیگر در یورش نظامیان صهیونیست

برپایی مراسم اعتکاف مسجد الاقصی با حضور 90 هزار فلسطینی/زخمی شدن 100 نفر دیگر در یورش نظامیان صهیونیست

از اعتکاف 90 هزار نفری در مسجدالاقصی تا زخمی شدن 100 نفر در یورش صهیونیست‌ها

از اعتکاف 90 هزار نفری در مسجدالاقصی تا زخمی شدن 100 نفر در یورش صهیونیست‌ها

 

3970294

 

 

 

captcha